in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi tur da barkewar fada a arewacin Mali
2016-07-23 14:03:14 cri
Sakatare Janar na MDD Ban Ki-moon, ya yi Allah wadai da barkewar sabon rikici a arewacin kasar Mali tsakanin bangarori biyu masu dauke da makamai, wadanda suka rattaba hannu kan amincewa da shirin tsagaita bude wuta.

A ranar Alhamis ne fada ya rincabe a garin Kidal, wani gari a yankin Hamada a arewacin Mali, tsakanin dakarun dake goyon bayan gwamnati, da 'yan tawayen Tuareg wadanda ke karkashin jagorancin Azawad Movements wato (CMA).

A wata sanarwa daga mai magana da yawun MDD ya ce, Ban, ya bayyana barkewar wannan fada a matsayin saba yarjejeniyar tsagaita bude wuta da aka kulla a watan Yunin shekarar 2015, kana ya bukaci shugabannin bangarorin biyu da su dauki matakan da za su tabbatar da maido da zaman lafiya a kasar. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China