in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta bukaci a tsagaita bude wuta yayin tunkarar wasannin Rio Olympic
2016-07-26 09:23:52 cri
Shugaban babban taron MDD Mogens Lykketoft ya bukaci kasashe mambobi da su tabbatar da tsagaita bude wuta a yayin da ake daf da fara wasannin Rio Olympic na 2016, da kuma Paralympics.

Tsagaita bude wuta a kasashen duniya mahalarta wasannin wadanda ke fama da rikice rikice wato tun daga kwanaki 7 kafin fara wasannin na Olympic zuwa kwanaki 7 bayan gama wasannin, zai taimaka wajen kara fahimtar juna da tabbatar da zaman lafiya a duniya baki daya.

Lykketoft, ya bukaci bangarorin da ba sa ga maciji da juna a duniya, da su amince da tsagaita bude wuta har zuwa karshen kammala wasannin na Olympic, kuma su lalibo bakin zaren warware dukkan wata takaddama cikin ruwan sanyi.

Za'a fara gudanar da wasannin Rio Olympic ne daga ranar 5 zuwa 21 ga watan Augusta, kana a gudanar da wasannin nakasassu na Olympics daga ranar 7 zuwa 18 ga watan Satumbar wannan shekara. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China