in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin ya yi kira ga kwamitin sulhun MDD da ya maida hankali ga yin shawarwari da tsaida kuduri tare
2016-07-20 13:49:38 cri
Zaunannen wakilin Sin dake MDD Liu Jieyi ya bayyana a jiya Talata 19 ga wata cewa, Sin ta nuna goyon bayan kwamitin sulhun MDD, game da ci gaba da kyautata hanyoyinsa na gudanar da ayyuka, tare da bukatar maida hankali kan gudanar da shawarwari da tsaida kuduri tare.

Liu Jieyi ya bayyana a gun muhawarar kwamitin sulhun kan batun hanyoyin gudanar da ayyuka cewa, kamata ya yi membobin kwamitin sulhun su tattauna tare, a wani mataki na kokarin cimma daidaito, yayin da kwamitin sulhun da hukumomin da yake jagoranta ke tsaida kuduri.

Ya ce idan bangarori daban daban na da bambancin ra'ayoyi, ya kamata a magance hakan ta hanyar tsaida kuduri, da neman cimma daidaito, da kiyaye ikon kwamitin sulhun.

Haka zalika kuma, Liu Jieyi ya yi kira ga kwamitin sulhun da ya kara azama wajen aikin shiga-tsakani, da hadin gwiwa, don magance amfani da hanyoyin kawo barazana, ko saba takunkumi da dai sauransu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China