in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bankin duniya ya sake duba karuwar hasashensa na farashin man fetur na shekarar 2016
2016-07-27 09:34:32 cri
Bankin duniya ya sake duba karuwar hasashensa na tashin farashin danyen man fetur, bisa ganin wata raguwa da wata bukata dake karuwa a tsawon watanni uku na biyu na shekarar 2016. A cikin rahotonta na baya bayan nan na watanni uku kan hangen kasuwar arzikin ma'adinai, hukumar mai bada rance dake da cibiya a birnin Washington ta bayyana cewa farashin gangar danyen mai zai cimma dalar Amurka 43 a shekarar 2016, wata karuwa idan aka kwatanta ga dalar Amurka 41 da aka yi hasashe a watan Afrilu.

Farashin man fetur sun karu da kashi 37 cikin 100 a tsawon watanni uku na biyu na shekarar 2016 dalilin wasu al'amura da dama da suka girgiza samar da man fetur, musamman ma wutar daji a Canada da lalacewar gine ginen man fetur a Najeriya. Muna nan muna jiran ganin farashin man fetur su dan kara karuwa a cikin rabin shekara na biyu na shekarar 2016, idan har harkokin samar da man fetur suka ragu, in ji John Baffes, babban jami'in da ya jagoranci wannan rahoto. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China