in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumomin ba da agaji na MDD sun kai tallafi ga dubban mutane a Sudan ta kudu
2016-07-15 10:25:50 cri
Jami'an MDD sun fada cewar asusun tallafawa kananan yara na MDD (UNICEF) da sauran hukumomin agaji sun fara kai agajin gaggawa domin ceto rayuwar dubban jama'a wadanda kazamin fada na makon jiya ya daidaita su a Juba, babban birnin Sudan ta kudu.

Fadan ya kaure ne a ranar 7 ga watan Yuli, tsakanin bangororin sojin da ba sa ga maciji da juna a yaririyar kasar, rahotanni sun ce sama da mutune 270 ne suka hallaka a lokacin tashin hankalin, ciki har da fararen hula 33, kuma sama da mutane 36,000 rikicin ya tilastawa ficewa daga gidajensu.

Wakilin hukumar UNICEF a Sudan ta kudu Mahimbo Mdoe, ya fada cewar, rikicin ya jefa mutane da yawa cikin halin kuncin rayuwa, kuma suna cikin matsananciyar bukatar tallafin abinci, da ruwan sha, da magunguna.

Mdoe, ya ce suna iyakar bakin kokarinsu wajen kai agajin, sai dai abu mafi muhimmanci shi ne yadda za su samu damar shigar da agajin ga mutanen dake cikin matsananciyar bukata, kasancewar akwai wuraren da ba su samun damar shiga.

Babban jami'in ofishin MDD ya fada cewar, a halin yanzu rikicin ya lafa a Juba, bayan shafe kwanaki 5 ana gwamza fada tsakanin bangarorin sojin kasar, sai dai akwai matsalar da jami'an kai agajin ke fuskanta na rashin samun damar shiga wuraren da aka killace mutanen da rikicin ya raba da muhallansu. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China