in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da ASEAN sun lashi takwabin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin tekun kudancin Sin
2016-07-25 19:03:33 cri
Kasar Sin da kungiyar kasashen kudu maso gabshin Asiya(ASEAN) sun sake nanata kudurinsu na kara kokari domin tabbatar da zaman lafiya , kwanciyar hankali da amincewa da juna a yankin tekun kudancin kasar Sin.

An kuma bayar da wata sanarwar hadin gwiwa bayan kammala ganawa tsakanin ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi da takwarorinsa daga kasashe 10 mambobin kungiyar ASEAN da ya gudana a babban birnin kasar Laos a lokacin taron ministocin harkokin wajen kungiyar ta ASEAN karo na 49.

Kasashen sun bayyana cewa, tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin tekun kudancin kasar Sin, shi ne babban muradun kasashe mambobin kungiyar da Sin har ma da duniya baki daya.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China