in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta tattauna tare da MDD kan aikin kula da sojojin wanzar da zaman lafiya
2016-06-25 12:30:47 cri
Tawagar hafsoshi karkashin babbar tawagar kasar Sin dake MDD ta sanar a ranar Jumma'a da cewa, wata tawagar jami'an kasar Sin ta ofishin harkar wanzar da zaman lafiya na ma'aikatar tsaron kasar ta kai ziyara MDD daga ranar 20 zuwa ta 24 ga watan da muke ciki, inda tawagar ta tattauna tare da bangaren MDD kan aikin kula da sojojin wanzar da zaman lafiya Sinawa.

A cikin wannan sanarwa, an ce MDD ta dora muhimmanci sosai kan tattaunawar da ake yi a wannan karo, inda Hervé Ladsous, mataimakin babban magatakardan Majalisar mai kula da aikin wanzar da zaman lafiya, da Atul Khare, mataimakin babban sakatare mai kula da aikin samar da abinci da kayayyaki ga sojojin wanzar da zaman lafiya, dukkansu sun gana da tawagar jami'an kasar Sin daya bayan daya.

Jami'an biyu na MDD sun nuna juyayi kan rasa ran wani sojan kasar Sin a kasar Mali, kuma sun nuna jaje ga sojojin Sinawa wadanda suka ji raunuka sakamakon harin da aka kai musu. Haka zalika sun kuma nuna yabo kan gudunmawar da kasar Sin take bayar wa ga aikin wanzar da zaman lafiya a kasashe daban daban.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China