in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ma'aikacin diflomasiyya na kasar Phillippines ya zargi kasashen Amurka da Japan da tsoma baki kan batun tekun kudancn Sin
2016-07-11 18:41:56 cri
A kwanan baya, Mr. Alberto Encomienda, tsohon babban sakataren cibiyar kula da harkokin teku ta ma'aikatar harkokin wajen kasar Phillippines ya bayyana cewa, kasashen Amurka da Japan suna yunkurin tilastawa kasar Sin da ta amince da hukuncin da kotun yanke hukunci ta kasa da kasa za ta yanke, yana mai cewa, wannan makarci ne da suka kitsa da nufin biyan muradunsu na siyasa.

Mr. Encomienda ya kara da cewa, dalilin da ya sa suka ingiza a yanke wannan hukunci shi ne suna tsammani za su samu moriya daga wannan hukunci, amma ainihin burin da suke son cimmawa shi ne biyan bukatunsu na siyasa. A ganin Alberto Encomienda, babu wata hujja da ta sa kasar Japan za ta tsoma baki kan batun tekun kudancin Sin. Amma a cikin 'yan shekarun da suka gabata, kasar Amurka ta taka muhimmiyar rawa wajen ganin an yanke hukunci kan maganar dake shafar yankin tekun kudancin Sin. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China