in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kai hari kan wani sansanin soja dake tsakiyar kasar Mali
2016-07-20 11:41:45 cri
Kakakin gwamnatin kasar Mali Mountaga Tall ya tabbatar a jiya Talata cewa, an kai kari kan wani sansanin sojan kasar dake Nampala a tsakiyar kasar, harin da ya haddasa mutuwar sojoji 12, yayin da mutane fiye da 30 suka ji rauni.

Bayan faruwar harin, shugaban kasar Mali Ibrahim Boubacar Keita ya gudanar da taron majalisar tsaron kasar, inda aka tattauna halin tsaro da ake ciki a kasar. Bayan taron, Tall ya bayyana yawan sojojin da suka mutu da wadanda raunata a sakamakon harin, amma bai bayyana yawan mutanen da suka kai harin da kuma wadanda suka mutu ko suka ji rauni ba.

A wannan rana, kungiyar dakarun da ke kare muradun Fulani ta kasar Mali ta sanar da kai wannan hari. Bayanai na cewa,wannan kungiya dai sabuwa ce a kasar. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China