in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban MINUSMA ya gabatar da sakon jaje game da rasuwar sojojin kiyaye zaman lafiya na MDD
2016-06-03 20:16:03 cri

Shugaban rundunar MDD mai aikin wanzar da zaman lafiya a kasar Mali wato MINUSMA Mahamat Saleh Annadif, ya ziyarci birnin Gao da ke arewacin kasar ta Mali a jiya Alhamis, inda ya gabatar da jaje ga sojojin MDDr da aka kaiwa harin ta'addanci a ranar 31 ga watan Mayun da ya shude. Ya kuma sake nanata aniyar MDD ta ci gaba da kiyaye zaman lafiya a kasar ta Mali.

A daren ranar 31 ga watan jiya ne aka kai harin ta'addanci har sau biyu, a sansanonin rundunar MINUSMA, inda mutane 4 suka rasa rayukansu, ciki had da wani Basine daya, yayin da wasu fiye da 10 suka jikkata. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China