in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
ECOWAS ta bukaci MDD da ta kara karfin tawagarta dake kasar Mali
2016-06-06 10:22:43 cri
Wasu kafofin watsa labaru na kasar Senegal, sun bayyana cewa kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka ta ECOWAS, ta zartas da wani kuduri na bukatar karfafa ayyukan tawagar kiyaye zaman lafiya ta MDD dake kasar Mali.

Ofishin ECOWAS din ya bayyana wannan bukata ne yayin taron koli, na kungiyar da aka gudanar a birnin Dakar na kasar Senegal a ranar Asabar, kudurin ya yi nuni da cewa, halin tsaro da ake ciki a kasar Mali ya kara tsananta, wanda hakan ya haifar da damuwa ga kasashen duniya, tare da kawo barazana ga yanayin tsaro a daukacin yammacin Afirka.

Kudurin ya kara da cewa, kungiyar ECOWAS tana nazartar yiwuwar kafa sojojin hadin gwiwar kasa da kasa, don yaki da ta'addanci a kasar Mali tare. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China