in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan ma'aikatan MINUSMA ya kai guda biyu ne
2016-06-04 12:26:47 cri
A ran Jumma'a 3 ga watan, tawagar wanzar da zaman lafiya ta MDD dake kasar Mali bisa matakai daban daban, wato MINUSMA ta fitar da wata sanarwa, inda ta bayyana cewa, yawan ma'aikatanta da suka rasa rayukansu sakamakon hare-haren ta'ddanci sau biyu da aka kai kan sansanin tawagar dake garin Gao da wani sansani daban na tawagar a ranar 31 ga watan jiya ya kai guda 2, ba guda 4 da aka sanar a kwanan baya ba.

Sanarwar ta ce, an tabbatar da cewa, ma'aikata guda biyu wadanda aka sanar da rasuwarsu a kwanan baya, sun ji raunuka masu tsanani, amma ba su rasu ba. Yanzu, ana yi wa wadannan ma'aikata 'yan kasar Mali jinya a asibitin Gao. Sabo da haka, adadin karshe na yawan ma'aikatan tawagar MINUSMA da suka rasu sakamakon wadannan hare-hare biyu ya kai guda biyu, tare da wasu ma'aikata hudu suka ji raunuka masu tsanani, sauran ma'aikata 11 sun samu raunuka marasa tsanani. Daga cikinsu, sansanin da sojojin kasar Sin masu wanzar da zaman lafiya a kasar Mali ke zaune ya samu asara mafi tsanani, inda wani sojan kasar Sin ya rasu, tare da wasu sojoji biyar da suka jikkata, daga cikinsu biyu na cikin mawuyacin hali mai tsanani sosai.

A ran 1 ga watan Yuni, kungiyar Al-Qaida ta Islamic dake yankin Maghreb ta sanar da daukar alhakin kai wadannan hare-hare biyu. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China