in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana neman kawar da cutar kanjamau nan da shekarar 2030
2016-07-19 11:25:40 cri
A jiya Litinin aka kaddamar da babban taron kasa da kasa kan cutar kanjamau mai karya garkuwar jiki karon 21, a birin Durban na kasar Afirka ta Kudu, inda za a kwashe kwanaki 5 don tattauna hanyoyin da za a bi don kawar da cutar daga doron kasa kafin shekarar 2030.

Taken taron shi ne, 'samun hakki na daidaituwa nan take'. An sanya wannan taken ne don nuna muhimmancin samar da isashen kudi don hana yaduwar cutar da kuma nazarinta, da jinyar wadanda suka kamu da cutar, da masu dauke da kwayoyin cutar cikin sauri, da daina nuna bambanci ga 'yan luwadi, da masu shan miyagun kwayoyi, da masu aikata karuwanci.

Mutane kimanin dubu 18 da suka hada da manyan jami'ai, da masana, da wakilan masu dauke da cutar kanjamau sun halarci taron.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China