Za a kafa jami'ar koyon fasahohin sadarwa ta farko ta Afirka a kasar Nijeriya
Jaridar THIS DAY da ake wallafawa a Nijeriya ta bayar da wani rahoto a jiya Litinin cewa, ministan harkokin sadarwa na kasar Adebayo Shittu ya bayyanawa 'yan jarida cewa, gwamnatin kasar tana shirin kafa jami'ar koyon fasahohin sadarwa ta nahiyar Afirka ta farko a Nijeriya don horar da kwararru a wannan fanni. Shittu ya bayyana cewa, wannan wani bangare ne na shirin raya fasahohin sadarwa da kasar Nijeriya ta bullo da shi, wanda za a gabatar da shi nan da wasu 'yan makwanni masu zuwa. (Zainab)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku