Shugaban 'yan sandan jihar Jimoh Ozi-Obeh ya bayyanawa 'yan jaridan kamfanin dillancin labaru na Xinhua cewa, yanzu 'yan sanda suna hadin gwiwa tare da sojojin ruwan kasar don tabbatar da ganin an sako mutanen da aka yi garkuwa da su.
Jami'in ya bayyana cewa, mutanen 5 da aka yi garkuwa da su sun hada da 'yan kasar Australia 2, dan kasar Afirka ta Kudu daya da kuma 'yan kasar Nijeriya biyu. Kana ya ce, an harba matukin motar da suke ciki har lahira.
Lamarin ya faru a ranar jiya Laraba da karfe 7 na safe a kan gadar Edundun. (Zainab)