Wakilin Sudan ta Kudu a kungiyar AU ya yi kira ga kasashen duniya da su kalubalanci jam'iyyar adawa da ta yi hadin gwiwa da gwamnatin kasar
Gwamnatin Sudan ta Kudu ta yi kira ga kasashen duniya da su matsa lamba ga jam'iyyar adawa, domin ta hada kai da gwamnatin kasar. Wakilin kasar Sudan ta Kudu a kungiyar AU, James Morgan shi ne ya bayyana hakan a jiya Laraba a yayin da yake halartar taron kolin kungiyar AU a birnin Kigali, babban birnin kasar Ruwanda,
James Morgan ya bayyana cewa, makomar Sudan ta Kudu ta dogaro ne ga jama'arta. A don haka kamata ya yi jam'iyyar adawa ta hada kai da gwamnatin kasar, domin a kara tabbatar da zaman lafiya a kasar.(Fatima)