in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An fara samun natsuwa a Juba
2016-07-15 11:21:23 cri
'Yan sandan kasar Sudan ta Kudu sun bayyana a ranar Alhamis cewa, an fara samun kwanciyar hankali a birnin Juba, fadar mulkin kasar Sudan ta Kudu, tun daga daren ranar 11 ga wannan wata, kuma ba a sake samun abkuwar wata matsala a fannin tsaro ba kawo yanzu.

A nasu bangaren, manyan kusoshin kasashen Afirka dake halartar taron kolin kungiyar tarayyar Afirka AU a Kigali na kasar Ruwanda, sun nuna damuwa kan yanayin da ake ciki a Sudan ta Kudu, tare da fatan ganin bangarorin kasar da ba sa ga maciji da juna zasu kawo karshen halin ja-in-ja da suke yi, da kiyaye yanayin tsagaita bude wuta, don maido da lumana a kasar tun da wuri.

Ban da haka kuma, masu halarta taron sun nuna yabo ga ma'aikatan wanzar da zaman lafiya a Sudan ta Kudu. Louise Mushikiwabo, ministar harkokin wajen kasar Ruwanda ta ambaci batun mutuwar wasu sojojin wanzar da zaman lafiya na kasar Sin a Sudan ta Kudu, inda ta ce, sojojin sun fi mai da hankali kan kare fararen hula maimakon tsaron kansu yayin da suka gudanar da aikinsu.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China