in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Karin wasu ma'aikatan kamfanonin Sin 260 sun janye daga Sudan ta Kudu zuwa Kenya
2016-07-14 10:35:44 cri
A jiya Laraba 13 ga wata, sauran ma'aikatan kamfanonin Sin a Sudan ta Kudu kimanin 260 sun janye daga birnin Juba, hedkwatar kasar zuwa birnin Nairobi, hedkwatar kasar Kenya ta jirgin sama.

Wakilin kamfanin ayyukan ketare na Sin (COVEC) a Sudan ta Kudu, Zhang Biao ya bayyana cewa, a wannan rana, jiragen sama 3 sun tashi daga Nairobi zuwa Juba, domin dauke da ma'aikatan kamfanonin Sin, daga bisani sun koma birnin Nairobi da daren wannan rana.

A daren ranar Talata 12 ga wata, ma'aikatan kamfanonin Sin sama da 70 sun tashi daga birnin Juba zuwa Nairobi. An ba da labarin cewa, kawo yanzu akwai wasu sauran ma'aikatan Sin a Sudan ta Kudu.

Tun daga ranar 8 ga wata, sojojin dake karkashin jagorancin shugaban kasar Sudan ta Kudu, Salva Kiir, da sojojin dake bin umurnin mataimakin shugaban kasar Riek Machar sun yi musayar wuta cikin tsanani a birnin Juba, wadda ta yi sanadiyyar mutuwar mutane 272. Filin jiragen saman kasa da kasa na Juba ya taba daina aiki sakamakon wannan rikici. A daren ranar 11 ga wata, Salva Kiir da Riek Machar sun bada umurnin tsagaita bude wuta tsakaninsu.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China