A ranar Alhamis da ta gabata, dakaru masu biyaya ga shugaban kasar Sudan ta Kudu Salva Kiir, da masu goyon bayan mataimahin shugaban kasar Riek Machar, sun yi dauki ba dadi a tsakaninsu a kewayen fadar shugaban kasar dake birnin Juba, rikicin da ya fantsama zuwa sauran wurare da kuma kusa da filin saukar jiragen sama daga bisani.
Bisa rahoton da jaridar Sudan Tribune ta bayar, an rawaito kwamishina mai kula da aikin agaji na kasar Sudan mista Ahmed Mohamed Adam na cewa, a kwanakin baya an samu karin 'yan gudun hijira da suke kwararowa cikin kasar Sudan daga Sudan ta Kudu, sai dai har yanzu ba a iya tabbatar da ainihin yawansu ba.
Jami'in ya jaddada yadda kasarsa take cikin shiri domin tinkarar duk wata matsalar da za ta iya kunno kai ga 'yan gudun hijirar kasar Sudan ta Kudu, idan rikici ya ki ci ya ki cinyewa a makwabciyar kasarsa.(Bello Wang)