in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tawaga ta 19 ta rundunar sojojin kiyaye zaman lafiya ta kasar Sin ta tashi zuwa Congo Kinshasa
2015-09-22 11:13:44 cri
Rukunin farko na tawaga ta 19 ta rundunar sojojin kiyaye zaman lafiya ta kasar Sin mai kunshe da sojoji 100 ta tashi daga filin jirgin sama na birnin Urumqi dake jihar Xinjiang na kasar Sin a daren ranar Litinin wato 21 ga watan nan zuwa kasar Congo Kinshasa don gudanar da ayyukan kiyaye zaman lafiya.

Tawagar ta hada da rukuni biyu na sojojin da kuna na ma'aikata da likitoci, adadin yawansu ya kai 225, kuma rukuni na biyu zai tashi a ranar 27 ga wannan watan.

Shugaban ofishin kula da harkokin kiyaye zaman lafiya na yankin soja na Lanzhou na kasar Sin ya bayyana cewa, a cikin shekara daya mai zuwa, sojojin kiyaye zaman lafiya za su zauna a yankin kudancin kasar Congo Kinshasa, wadanda za su gudanar da ayyukan gina hanyoyi da gadaje, ayyukan samar da ruwan sha da wutar lantarki da kiwon lafiya da sauran ayyukan jin kai a kasar. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China