in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU na bada fifiko ga ilimi domin kawar tashe tashen hankali da bambance bambance
2016-07-16 12:13:37 cri
Bambance bambancen dake nasaba tsakanin maza da mata, yi wa mata kaciya, yi wa mata fyade da makamantan haka, wahalhalun samun ilimi da mallakar filaye, sun kasance wasu daga cikin taken batutuwan da shugabar reshen "Mata, bambance bambance tsakanin maza da mata da kuma ci gaba" na kwamitin kungiyar tarayyar Afrika (AU), madam Mahawa Kaba Wheeler, ta mai da hankali a kai a yayin wani taron manema labarai da ta jagoranta a Kigali na kasar Rwanda a ranar Jumma'a da yamma.

A cewar nazarinta, jahilci shi ne gishikin dake haddasa tashe tashen hankali da bambance bambance da ake nuna mata. Dalilin hake ne take baiwa ilimi babban muhimmanci wajen bunkasa 'yancin mata a Afrika.

Kuma a bangaren tarayyar Afrika, muhimmin makamin bunkasa ilimi shi ne yarjejeniyar Maputo. Karin takarda ga kundin Afrika kan 'yancin dan Adam, da aka rattaba hannu kansa a cikin watan Julin shekarar 2003 a yayin babban taron shugabanni da gwamnatocin kasashen Afrika a birnin Maputo na Mozambique.

Daya daga cikin sauye sauye na wannan yarjejeniyar Maputo, kamar yadda madam Wheeler ta tunatar shi ne muhimmancin da yake baiwa ilimi bisa ayyarsa ta 12 kan tilastawa masu fada a ji, na samarwa mata damar samun aiki da shiga harkokin kasa cikin adalci kuma ba tare da nuna bambanci ba. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China