in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen Afrika sun yi kira da a warware rikicin Sudan ta Kudu daga tushe
2016-07-13 11:05:11 cri
Wakilan dindindin na kasashen kungiyar tarayyar Afrika (AU) sun yi kira ga bangarori masu gaba da juna na kasar Sudan ta Kudu da su kawo karshen wannan rikici nan take. Wakilan sun yi wadannan kalamai a ranar Talata a wajen babban taron kungiyar AU karo na 27 dake gudana a yanzu haka a Kigali, babban birnin kasar Rwanda.

Kasar Rwanda dai na karbar bakuncin dandalin kungiyar AU daga ranar 10 zuwa 18 ga watan Yuli bisa taken "Shekarar 2016, shekarar 'yancin dan adam, tare da maida hankali musammun ma kan 'yancin mata". Da yake tsokaci gaban manema labarai a zaman taro da aka saba karo na 32 na kwamitin wakilan dindindin (PRC), Cherif Mahamat Zene, jakadan kasar Chadi dake Habasha, kana wakilin dindindin na kungiyar AU, yayi kira ga shugabannin Sudan ta Kudu dasu bullo da hanyar warware wannan rikici daga tushensa. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China