in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a zabi shugaban AU a taron kungiyar da za a gudanar a Kigali
2016-07-03 13:10:16 cri
Kungiyar tarayyar Afrika AU zata zabi shugaba da mataimakinsa, kuma wannan na daga cikin manyan ayyukan da za a gudanar a wajen taron kolin kungiyar ta AU da zai gudana a Kigali babban birnin kasar Rwanda tsakanin ranakun 10 zuwa 18 ga watan da muke ciki.

Taken taron na wannan karo shine, "shekarar hakkin dan Adam, musamman lura da hakkin 'yan mata".

Kungiyar AU, ta sanar da hakan ga wakilan wasu kungiyoyin jama'a da na kasa da kasa, gami da yin bayani kan manyan batutuwan da za a tattauna a wajen taron karo na 27 na shugabannin kungiyar, kamar yadda aka bayyana a cikin sanarwar kungiyar a jiya Asabar.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China