in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta bukaci shugabanni su bullo da dabarun bunkasa kasuwanci a nahiyar Afrika
2016-07-15 09:54:53 cri
Kwamitin kungiyar tarayyar Afrika (AUC) ya bukaci shugabanni da kwararru na Afrika da su gaggauta aiwatar da shirin CFTA na habaka kasuwanci maras shinge a nahiyar domin cimma wa'adin shirin nan da shekarar 2017.

Fatima Haram Acyl, kwamishiniyar AU mai kula da kasuwanci da masana'antu, ta yi wannan kira ne a jiya Alhamis a yayin taron kolin AU karo na 27 a Kigali, babban birnin Rwanda.

Taron wanda ake gudanar da shi tsakanin ranakun 10 zuwa 18 ga wannan wata, mai taken "shekarar 2016 ta kare hakkin dan adam, da ba da fifiko ga hakkin mata".

Da take jawabi ga taron shugabannin kungiyar AU karo 29, Haram Acyl, ta shedawa 'yan jaridu cewar, kamar yadda kungiyar ta kuduri aniya kan muradunta na 2063 da sauran shirye-shirye, ta ce dole ne shugabannin Afrika da kwararru su duba yiwuwar cimma muradun kasuwanci maras shinge a nahiyar wanda wa'adinsa zai cika a shekara mai zuwa.

Kana ta bukaci ministocin kasuwanci na kasashen Afrika da su hanzarta cimma matsaya kafin karewar wa'adinsa a shekarar 2017. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China