in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sassauta ka'idoji game da cinikayya zai habaka tattalin arzikin Afrika
2016-07-12 10:30:08 cri
Mahalarta taron kolin kungiyar tarayyar Afirka AU karo 27 da ake gudanarwa a Kigali babban birnin kasar Rwanda, sun bayyana cewa sassauta dokoki game da yadda ake gudanar da cinikayya a tsakanin kasashen Afrika, zai matukar haifar da bunkasuwar tattalin arzikin nahiyar.

Taron na bana wanda ake gudanarwa tsakanin ranakun 10 zuwa 18 ga wannan wata, taken taron na shekarar 2016 shi ne, "shekarar Afrika ta kare hakkin dan adam, tare da bada fifiko ga hakkin mata".

Babban jami'in kwamitin wakilai PRC, kuma jakadan jamhuriyar Chadi a Habasha, wakili na musamman a AU, Cherif Mahamat Zene, ya fada cewa sassauta dokoki game da cinikayya zai bunkasa cigaba wajen shigo da kayayyaki da fitar da dasu zuwa kasashen waje a nahiyar ta Afrika.

Ya kara da cewar babban kalubalen dake addabar hada hada tsakanin kasashen nahiyar shi ne, tsauraran dokokin dake haifar da koma baya ga sha'anin cinikayya a tsakanin kasashen na Afrika, don haka ya jaddada bukatar kawo sauyi ga wannan batu.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China