in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan kasar Sin ya aika da sakon jajantawa ga takwaransa na kasar Faransa kan harin ta'addancin da aka kai wa birnin Nice
2016-07-15 17:20:59 cri

Firaministan kasar Sin Li Keqiang ya aika da sakon jajantawa ga takwaransa na kasar Faransa Manuel Valls kan harin ta'addanci da aka kai a bnirnin Nice, kuma ya yi Allah wadai da masu kai jari tare da nuna juyayi ga mutanen da suka mutu, daga nisani kuma, ya jajanta wa iyalan wadannan mutane.

Mr. Li Keqiang ya bayyana cewa, gwamnatin Sin da kuma jama'ar kasar sun nuna jajantawa ga jama'ar kasar Faransa, za ta dauki matsayi iri daya tare da jama'ar Faransa, tana son kara yin hadin gwiwa tare da kasar Faransa da kuma sauran kasashen duniya domin yaki da ta'addanci da kiyaye zaman lafiya a duniya.(Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China