in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rukunin aiki na Sin ya tashi zuwa kasar Sudan ta Kudu
2016-07-14 10:42:45 cri
Rukunin aiki na kasar Sin ya tashi daga birnin Beijing zuwa kasar Sudan ta Kudu a jiya Laraba 13 ga wata don nuna gaisuwa ga sojojin kiyaye zaman lafiya na kasar da suka raunata yayin da suke gudanar da aiki, da dawo da gawawwakin sojojin da suka mutu da sojojin da suka ji rauni zuwa kasar Sin.

Hukumar harkokin watsa labaru ta ma'aikatar tsaron kasar Sin ta bayyana cewa, mukadashin shugaban ofishin harkokin kiyaye zaman lafiya na ma'aikatar Su Guanghui ya jagoranci rukunin.

Rukunin zai nuna gaisuwa ga sojojin kiyaye zaman lafiya na kasar Sin dake birnin Juba na kasar Sudan ta Kudu, tare da yin bincike ayyukan kiyaye tsaro a wurin da aka kai hari, da bada jagoranci ga sojojin kiyaye zaman lafiya wajen gudanar da aiki, da yin bincike kan yanayin sojojin da yanayin tsaro da ake ciki a can, da yin hadin gwiwa tare da tawagar musamman ta MDD dake kasar Sudan ta Kudu da gwamnatin kasar Sudan ta Kudu wajen daukar matakai don tabbatar da tsaron sojojin kiyaye zaman lafiya da gudanar da ayyukan kiyaye zaman lafiya yadda ya kamata.

A ranar 10 ga wannan wata, an kai harin bom kan wata motar sojojin kiyaye zaman lafiya na kasar Sin dake kasar Sudan ta Kudu yayin da suke gudanar da aiki a sansanin MDD dake kasar Sudan ta Kudu, wanda ya haddasa mutuwar sojojin Sin biyu, yayin da biyar suka ji rauni. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China