in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU za ta kaddamar da fasfo na zamani a watan Yuli
2016-06-14 19:31:23 cri
Kungiyar tarayyar Afirka wato AU, tana shirin kaddamar da fasfo na zamani da ake kira e-passport a yayin taron kolinta na gaba da zai gudana a watan Yulin wannan shekara a birnin Kigali,fadar mulkin kasar Rwanda.

Kungiyar wadda ta bayyana hakan a yau Talata cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai, ta ce rukunin farko na wadanda za su fara amfani da fasfon sun hada da shugabannin kasashe da gwamnatoci na kungiyar,ministocin harkokin waje,wakilan din-din-din na kasashe mambobin kungiyar da ke zaune a hedkwatar kungiyar a birnin Addis Ababa na kasar habasha.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China