A cikin wata sanarwar da aka gabatar ta gidan talebijin na Sudan ta Kudu, ministan sadarwa na Sudan ta Kudu, Michael Makuei Lueth ya bayyana cewa, duk hafsoshin sojojin kasar za su bi wannan umurni, su kula da sojojinsu, tare da ba da kariya ga fararen hula da dukiyoyinsu.
A wannan rana da dare, mataimakin shugaban kasar, Riek Machar ya bayyana ta bakin kakakinsa cewa, dakarun dake karkashin jagorancinsa su ma za su tsagaita bude wuta a wannan rana da dare da misalin karfe takwas.(Fatima)