in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kungiyar tarayyar Afrika (AU) ya bukaci da a dakatar da bude wuta a Sudan ta Kudu
2016-07-12 10:23:26 cri
Ma'aikatar harkokin wajen kasar Chadi ta bayar da wata sanarwa a jiya Litinin, inda ta ce, shugaban kasar Chadi Idriss Deby Itno, kana kuma shugaban kungiyar tarayyar Afrika (AU) a wannan karo, ya yi kira a ranar Litinin ga bangarorin dake gaba da juna a Sudan ta Kudu, da su dakatar da bude wuta.

Sanarwa ta ce, shugaba Deby Itno ya bayyana damuwarsa game da sake barkewar tashe tashen hankali a Sudan ta Kudu tare da kuma yin kira da a dakatar da bude wuta nan take.

Bisa bukata ta dalili, a matsayin shugaba mai ci na kungiyar AU, ya bukaci Alpha Oumar Konare wakilin dindindin na kungiyar AU a Sudan ta Kudu, da ya je wannan kasa domin ya isar da sakon damuwarsa kan bangarori masu gaba da juna.

A ranar Litinin da yamma, shugaban Sudan ta Kudu Salva Kiir ya sanar da tsagaita bude wuta, 'yan kwanaki kadan bayan wani gumurzu tsakanin sojojin gwamnatin kasar da dakaru masu biyayya ga mataimakin shugaban kasa na farko Riek Machar. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China