in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta fitar da farar takarda game da yadda za a warware takaddamar dake tsakaninta da kasar Philippines
2016-07-13 20:00:13 cri
A yau ne gwammatin kasar Sin ta fitar da farar takarda domin bayyana matsayinta, wadda ke kira a sasanta takaddamar da ke tsakaninta da kasar Philippines game da tekun kudancin kasar Sin ta hanyar sasantawa.

Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Sin Liu Zhenmin shi ne ya bayyana hakan yau, a yayin da yake gabatar da wannan takarda a taron manema labarai da ya gudana a nan birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin.

Ya ce, matakin da kasar Phillippines ta dauka babu abin da zai haifar illa kara tsananta takaddamar da ke tsakanin kasashen biyu kan batun tekun kudancin kasar ta Sin.

Ita dai wannan takarda mai take, "Kasar Sin tana kan matsayinta na daidaita wannan batu ta hanyar sasanta takaddamar dake tsakaninta da kasar Philippines kan batun tekun kudancin kasar Sin" an wallafa ta ne kwana guda bayan da wata kotu ta yanke hukunci kan wannan batu bisa bukatar tsohuwar gwamnatin kasar Philippines.

Liu ya bukaci sauran kasashe da kada su yi amfani da wannan dama wajen yiwa kasar Sin barazana. Kasar Sin tana fatan sauran kasashe za su yi kokarin tabbatar da zaman lafiya da kwancikyar hankali a yankin tekun kudancin kasar Sin, maimakon barin yankin ya fada cikin yaki.

Bugu da kari, mataimakin ministan ya bayyana cewa, kasar Sin ta dage 'yancin yin zirga-zirga ta sama a yankin tsaron da ta shata a yankin, saboda barazanar da yankin yake fuskanta a halin yanzu. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China