in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar lauyoyi ta Hongkong na Sin ta nuna tababa ga ikon yanke hukunci na hukumar yanke hukunci ta Hague kan batun tekun kudancin Sin
2016-07-12 13:30:43 cri
A kwanan baya, kungiyar lauyoyi ta yankin Hongkong na Sin mai suna asusun musayar ilmin doka na Sin da Australia ta mika takardar ra'ayi ga hukumar yanke hukunci ta Hague ta Netherlands, inda asusun na ganin cewa, hukumar Hague ba ta da ikon kulawa da batun yanke hukunci ga batun tekun kudancin kasar Sin da Philippines ta gabatar da kanta.

Shugaban kwamitin gudanarwa na asusun musayar ilmin doka na Sin da Australia, kana babban lauya mai izni na babbar kotun Hongkong, Ma Enguo ya bayyana a gun taron manema labaru da aka shirya a jiya Litinin cewa, batun tekun kudancin kasar Sin, wani irin rikici ne dake shafar ikon mallakar tsibiran yankin tekun da sauransu tsakanin Sin da Philippines. Bisa yarjejeniyar dokar teku ta MDD, da zarar rikicin yankin teku ya shafi ikon mallakar kasa, sai hukumar yanke hukunci kan batun yankin teku ba ta da ikon kulawa a kai.

Mataimakin shugaban asusun, lauya Qian Zhiyong ya nuna cewa, Philippines ta fidda wannan hukunci da kanta, Sin ba za ta karba ba, ba za ta shiga batun ba. Idan Sin ba za ta shiga wannan batu ba, duk ayyukan da za a yi ba za su dace da dokoki ba.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China