in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar ingiza dinkuwar duk kasar Sin gaba daya cikin lumana ta Afirka ta nuna goyon baya ga gwamnatin kasar Sin
2016-07-10 13:06:31 cri
Dangane da batun yanke hukunci kan takaddama game da tekun kudancin Sin wanda gwamnatin kasar Phillippines ita kadai ta gabatarwa kotun yanke hukunci ta kasa da kasa, jiya Asabar kungiyar ingiza dinkuwar duk kasar Sin gaba daya cikin lumana ta Afirka ta fitar da wata sanarwa, inda ta bayyana cewa, kotun yanke hukunci ta kasa da kasa ba ta da ikon sauraron irin wannan magana, sakamakon haka, kowane irin hukuncin da za ta yanke ba zai yi aiki ba, Sinawa wadanda suke aiki a kasashen Afirka dukkansu sun nuna goyon baya ga matakan da gwamnatin kasar Sin ta dauka na kiyaye ikon mulkin yankunan kasar da moriyarta dake yankin teku.

Wannan sanarwa ta nuna cewa, tun fil azal, tsiriban Nansha yankunan kasar Sin ne. A cikin dogon lokaci bayan yakin duniya na 2, babu kasancewar takkadama kan yankin tekun kudancin Sin. Amma a shekaru 70 na karnin da ya gabata, an gano arzikin man fetur da iskar gas a yankunan tekun kudancin Sin, sakamakon haka, wasu kasashe ciki har da kasar Phillippines suka mamaye wasu kananan tsibiran kasar Sin dake yankin teku na Nansha ba tare da samun izini ba, wannan shi ne asalin dalilin da ya sa aka samu takkadama kan yankin tekun kudancin Sin.

Wannan sanarwa ta kuma zargi gwamnatin kasar Phillippines da kin yin amfani da darusan "yarjejeniya kan dokokin dake shafar teku ta MDD", har ma ta gabatar da maganar neman yanke hukunci kan yankin tekun kuddancin Sin ita kadai a kokarin samun ikon mulkin tsibiran da ta mamaye a da ba bisa doka ba, da kuma musunta ikon halal da moriyar halal na kasar Sin a yankin tekun kudancin Sin.

Daga karshe, sanarwar ta bayyana cewa, wasu kasashe suna neman mayar da kasar Sin saniyar ware bisa wannan maganar neman yanke hukunci kan batun yankin tekun kudancin Sin, amma ba za su cimma burinsu ba. Yanzu yawan kasashen da suke goyon bayan matsayin da kasar Sin take dauka yana ta karuwa. Ya kamata kasashen da suke yankin tekun kudancin Sin su daidaita matsalolin dake kasancewa a tsakaninsu da kasar Sin ta hanyar yin shawarwari kai tsaye cikin lumana a tsakaninsu da kasar Sin. Kasar Sin da kasashen Asiya, suna iya tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin tekun kudancin Sin ta hanyar yin hadin gwiwa tsakaninsu. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China