in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta bayyana alfanun rigakafin barkewar rikici a yammacin Afrika da yankin Sahel
2016-07-12 10:33:35 cri
Babban wakilin MDD na musamman Mohamed Ibn Chambas, ya fada a jiya Litinin cewa, daukar matakan kariya daga barkewar rikice rikice nada matukar muhimmanci, idan aka yi la'akari da yadda rikice rikicen ya jefa rayuwar mutane kusan miliyan 4 da rabi cikin mawuyaci hali da kauracewa matsugunan su a yakin Sahel kadai.

Chambas, wanda kuma shi ne shugaban ofishin MDD na yammacin Afrika da yankin Sahel, ya bayyanawa kwamitin sulhu na MDD game da halin da ake ciki a yammacin Afrika da Sahel cewa, matsalolin da suka shafi rashin aikin yi, da rashin adalci sun taimaka wajen haddasa yawaitar kungiyoyin tada kayar baya a yankunan.

Ya bukaci kasashen duniya su hada karfi da karfe wajen rigakafin barkewar rikice rikice da kuma dakile rikicin tun a matakan farkon.

Yace kasashen yammacin Afrika da yankin Sahel, dole ne su maida hankali wajen samar da hanyoyin tattara bayanan sirri domin yaki da kungiyoyin tada kayar baya kamar su Boko Haram, wadanda suke kaddamar da hare haren ta'addanci a kasashen Najeriya da Nijer da Kamaru.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China