Cikin sanarwar da ofshin watsa labarai na ma'aikatar tsaron kasar Sin ya bayar, an ce an kai hari ga sojojin ne lokacin da suke gudanar da aikin tsaron mafakar 'yan gudun hirjira. A nata bangaren, rundunar sojan kasar Sin ta nuna kaduwa game da faruwar hari, kuma ta yi Allah wadai da mummunan harin da aka kai. Bangaren rundunar ta nuna juyayi ga rasuwar sojanta, kuma ta jajantawa iyalan wadanda suka samu raunuka.
Bayan abkuwar harin, rudunar sojojin kasar Sin ta kaddamar da shirin ko ta kwana nan take, kana ana kokarin ceton rayukan sojojin da suka ji rauni, gami da kara tsaurara matakan tsaro a wurin.(Bello Wang)