in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhun MDD ya mika ta'aziya dangane da sojojin kiyaye zaman lafiya na Sin da suka mutu a Sudan ta Kudu
2016-07-11 16:51:44 cri
A jiya Lahadi ne, kwamitin sulhun MDD ya ba da wata sanarwa, inda a ciki ya nuna tausayi tare da jajantawa iyalan sojojin kiyaye zaman lafiya na Sin da suka rasa rayukansu a Sudan ta Kudu sakamakon rikicin da ya barke a cikin rundunar sojan kasar Sudan ta Kudu.

A cikin sanarwar, da babbar murya kwamitin sulhun MDD ya yi Allah wadai da wannan danyen aiki, yana mai jaddada cewa, kai hari kan farare hula da sansanin hukumomin MDD da ma'aikatan MDD tamkar aikata laifin yaki ne. Don haka dole a gurfanar da wadanda suka kai harin a gaban kotu.

Dadin dadawa, a cikin sanarwar, kwamitin sulhun MDD ya jaddada muhimmancin ba da kariya ga ma'aikatan kiyaye zaman lafiya na MDD da wuraren MDD da ke kula da lafiyar fararen hula a wurin. Ya ce kwamitin sulhun zai yi la'akari da kara tura sojoji zuwa tawagar musamman ta MDD dake Sudan ta Kudu. (Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China