'Yan gudun hijiran kasar Sudan ta Kudu fiye da dubu 40 sun tsera zuwa yankin Darfur dake Sudan
A jiya ne ofishin kula da harkokin jin kai na MDD(OCHA) da hukumar kula da kaurar jama'a ta duniya(IOM) suka gabatar da rahoto game da ayyukan jin kai a kasar Sudan ta Kudu, inda suka bayyana cewa, tun daga shekarar bana, 'yan gudun hijira daga kasar Sudan ta Kudu fiye da dubu 47 aka tilastawa tsallakawa yankin Darfur dake kasar Sudan. Inda kimanin mutane 500 a kowa ne yini ke shiga kasar Sudan daga kasar Sudan ta Kudu. (Zainab)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku