in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan gudun hijirar kasar Sudan ta Kudu da yawa sun shiga cikin kasar Sudan
2016-05-21 13:30:08 cri
A jiya Jumma'a 20 ga wata, ofishin kyautata harkokin jin kai na MDD a Sudan ya ba da rahoton cewa, daga watan Janairun bana zuwa yanzu, dalilin tabarbarewar yanayin da ake ciki da karancin abinci a kasar Sudan ta Kudu, 'yan gudun hijira da yawa sun fice daga kasar zuwa wasu yankunan kasar Sudan.

Rahoton ya ce, ya zuwa ranar 12 ga watan Mayu, kimanin mutanen Sudan ta Kudu dubu 69 sun shiga kasar Sudan ta yankin arewacin iyakar kasa, a ciki kimanin mutane dubu 46 sun isa jihar East Darfur. Rikice-rikice, da karancin amfanin gona, da raguwar darajar kudi, da kuma hauhawar farashin abinci, sun janyo ficewar mutane da dama daga Sudan ta kudu

A ranar 17 ga watan Maris na bana, gwamnatin Sudan ta yanke shawarar kebe mutanen Sudan ta Kudu dake zama a Sudan a matsayin 'mutanen ketare', wadanda za su yi zama a Sudan kamar yadda sauran kasashen waje suke. Kuma za a dauki matakai bisa doka kan duk mutanen Sudan ta Kudu da suka shiga kasar Sudan ba tare da takardar izini ba.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China