Ministan harkokin waje na kasar Senegal Mankeur Ndiaye ya bayyana a kwanan baya cewa, kasar Senegal ta nuna goyon bayan kasar Sin wajen daidaita batun tekun kudancin Sin ta hanyar yin shawarwari tare da kasar Philippines, domin kiyaye zaman lafiya da tsaro a yankin.
Mankeur Ndiaye ya bayyana cewa, kasashen Sin da Philippines sun taba cimma matsaya daya a kan batun tekun kudancin Sin a lokacin da. Don haka kasar Senegal ta yi kira ga kasashen da abin ya shafa da su daidaita batun bisa matsaya daya da suka cimma, ta hanyar yin shawarwari, a kokarin kiyaye zaman lafiya da tsaro a yankin.