A yayin da Jeronimo Osa Osa Ecoro ke zantawa da wakilin kamfanin dillancin labaru na Xinhua na kasar Sin, ya bayyana cewa, kasar Philippines ta gabatar da karar yanke hukunci kan batun tekun kudancin Sin bisa kashin kanta, lallai wani lamari ne da bai dace ba, kana wannan matakin da ta dauka zai kawo cikas ga shimfida zaman lafiya a yankin. A madadin jam'iyyarsa, Jeronimo Osa Osa Ecoro ya yi kira ga kasar Philippines da ta yi shawarwari tare da Sin wajen daidaita batun ta hanyar siyasa, domin kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.(Lami)