in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Na'urar ta biyu ta Tiangong-2 ta kasar Sin ta isa cibiyar harba tauraron dan adam ta kasar
2016-07-10 12:31:05 cri
Na'ura ta biyu ta Tiangong-2 ta kasar Sin, wacce ake sa ran 'yan sama jannati biyu za su iya yin aiki da yin zama a ciki a sararin samaniya har tsawon kwanaki 30 ta riga ta isa cibiyar harba tauraron dan Adam ta kasar, wato Jiuquan Satellite Launch Center.

A sanarwar da ofishin kula da kimiyyar binciken sararin samaniyar ta kasar Sin ya gabatar, ya ce an tura na'urar gwaje gwajen ne daga birnin Beijing tun a ranar Alhamis ta jirgin kasa, kuma ta isa cibiyar a jiya Asabar, kana wannan ya nuna cewar an zo mataki na gaba na fara aiwatar da shirin harba na'urorin binciken sararin samaniyar ta Tiangong-2 da Shenzhou-11.

Sanarwar ta kara da cewar, za'a fara harhada na'urar ne da kuma gwada ta a cibiyar, kafin daga bisani a harba na'urar wanda ake sa ran gudanarwa a watan Satumba. (Ahamd Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China