in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin shugaban kungiyar kungiyar AU ya goyi bayan matsayin Sin kan batun tekun kudancin kasar
2016-06-03 11:24:05 cri
Mukaddashin jakadan Sin na tawagar kasar a kungiyar AU Chen Xufeng ya gana da mataimakin shugaban hukumar zartarwar kungiyar AU Erastus Mwencha a kwanakin baya, inda suka yi musayar ra'ayoyi kan hadin gwiwa a tsakanin Sin da AU da sauran batutuwan da suke sa lura tare.

Chen Xufeng da Mwencha sun tattauna ayyukan hadin gwiwa a tsakanin bangarorin biyu ta fannonin raya hanyoyin jiragen kasa da motoci da jiragen sama da raya masana'antu a kasashen Afirka da kafa cibiyar kula da cututtuka ta Afirka.

Mwencha ya nuna yabo ga Sin kan gudummawar da ta samar da kuma sabon sakamakon hadin gwiwar da bangarorin biyu suka cimma, yana mai imanin cewa, bangarorin biyu za su kara zurfafa dangantakar hadin gwiwar.

Game da batun tekun kudancin kasar Sin, Mwencha ya nuna goyon baya ga matsayin Sin kan wannan batu, kana ya yi kira ga kasashen da abin ya shafa kai tsaye da su samar da damar yin shawarwari da juna, da warware matsalar ta hanyar yin shawarwari cikin lumana bisa dokokin kasa da kasa. Mwencha ya jaddada cewa, kamata ya yi kasashen da abin ya shafa da su bi ka'idojin sanarwar bangarori daban daban da batun tekun kudancin Sin ya shafa,tare da warware matsalar ta hanyar yin shawarwari cikin lumana, da kara yin imani da juna, a kokarin tabbatar da zaman lafiya a tekun kudancin kasar Sin. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China