in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalisar koli ta al'amurran addinin muslunci a Najeriya ta sanar da Laraba a matsayin ranar Idin karamar sallah
2016-07-05 16:13:54 cri
Majalisar koli game da al'amurran addinin musulunci ta Najeriya (NSCIA) ta sanar da gobe Laraba 6 ga watan Yuli a matsayin ranar Idin karamar sallah a fadin kasar.

Mai alfarma sarkin musulmi, kuma shugaban majalisar koli ta addinin musulunci Sultan na Sokoto, Alhaji Sa'ad Abubakar III, shi ne ya sanar da hakan, ya ce ba'a samu ganin jinjirin watan Shawwal ba a dukkan fadin Najeriya.

Sakamakon hakan, ya umarci al'ummar musulmin kasar dasu gudanar da azumi a yau Talata, kuma su gudanar da Idin karamar sallah a gobe Laraba.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China