in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tsohon shugaban Najeriya ya bukaci a samar da kudi bai daya a yammacin Afrika
2016-07-05 09:58:06 cri
Tsohon shugaban Najeriya Olusegun Obasanjo, ya ce samar da kudi bai daya a kasashen yammacin Afrika zai bunkasa ci gaban tattalin arzikin kasashen yanki da kuma kawo gagarumin ci gaba a yankunan.

Obasanjo ya yi kiran ne a Litinin a lokacin zantawa da shugaban kungiyar raya ci gaban tattalin arzikin kasashen Afrika ta yamma (ECOWAS), Marcel de Souza, a Abeokuta dake kudu maso yammacin kasar Najeriya.

Ya ce lokaci ya yi da kasashen za su fara amfani da kudi na bai baya, domin a cewarsa zai yi matukar habaka ci gaban tattalin arzikin mambobin kungiyar ta ECOWAS.

Ya kara da cewar, samar da kyakkyawan yanayin ci gaban tattalin arziki na ECOWAS zai tallafawa wajen rage matsalolin rashin ayyukan yi a tsakanin matasan wadannan kasashen, zai kuma tabbatar da bunkasuwar kasashen yammacin Afrika baki daya.

Obasanjo ya bukaci mambobi kasashen da su bullo da sabbin hanyoyin ci gaban kasashensu wanda ya zarta na batun zirga zirgar kayayyaki tsakanin kasahen, kana ya gargadi shugabannin kasashen nahiyar ta Afrika da cewar, rashin kulawa da ci gaban matasa wajen samar musu ayyukan yi babbar barazana ce ga zaman lafiyar kasashen. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China