in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Togo za ta karrama sojojin wanzar da zaman lafiya na MDD 'yan kasarta da aka kashe a Mali
2016-07-05 09:47:26 cri
Wani bikin karramawa na kasa zai gudana a ranar Jumma'a mai zuwa ga sojojin wanzar da zaman lafiya na MDD guda biyar 'yan kasar Togo da aka kashe a ranar 29 ga watan Mayu a Sevare, dake arewacin Mali, in ji gwamnatin Togo a ranar Litinin.

Sojojin biyar sun mutu a yayin wani kwanton bauna a Sevare dake kusa da birnin Mopti dake tsakiyar kasar Mali a lokacin da suke cikin wani rukunin zaratan sojojin sintiri da ba da tallafi da kuma rukunin dakaru na hudu. Wannan karramawar za ta kasance wata dama ga 'yan kasar Togo da su yi addu'o'i domin kwanciyar mamatan biyar dake aikin kare zaman lafiya.

Togo ta tura kusan sojoji dubu guda a kasar Mali a cikin tsarin tawagar wanzar da zaman lafiya ta MDD dake kasar Mali (MINUSMA), dake da sansaninsu a Douinza tare da wasu runkunoni a Gosso da Sevare. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China