in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
EU ta yi alkawarin karfafa dangantaka da yammacin Afrika wajen yaki da ta'addanci
2016-06-25 13:16:14 cri
Zaman taro na kwamitin shata manyan manufofi (COS) karo na uku na kungiyar tarayyar Turai game da yammacin Afrika ya kammala a ranar Jumma'a a birnin Lome tare da wata niyyar kungiyar ta EU kan matakan da suka dace, don yaki da ta'addanci, annobar dake kawo barazana ga zaman lafiya da tsaron shiyyar da kasa da kasa.

Wannan haduwa ta kwanaki biyu wacce ta samu halartar masu fada a ji na kasashen shiyyar, ta taimaka wajen daukar matakai da kudurori domin cigaba da aiwatar da tsarin nuni na shiyyar (PIR) na asusun cigaba na kungiyar tarayyar Turai na goma (10e FED) da kuma shirye shiryen aiwatar da shirin FED na goma sha daya (11e FED).

Bisa la'akari kan cewa babu wani cigaba idan babu zaman lafiya, tsaro da kwanciyar hankalin shiyyar, EU ta nuna damuwa game da karuwar ayyukan ta'addanci a yammacin Afrika, musammun ma a kasashen Burkina Faso, Cote d'Ivoire, Nijar da Najeriya tare da bayyana goyon bayanta ga wadannan kasashe da matsalar ta shafa.

Haka kuma, kungiyar tarayyar Turai ta bayyana gamsuwarta kan cigaban da aka samu wajen tabbatar da zaman lafiya a shiyyar tare da jaddada niyyarta na yaki da wannan matsala da matakan da suka dace, yaki da wannan annoba dake kawo barazana ga zaman lafiya da tsaron shiyyar da ma kasa da kasa. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China