in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta ta bukaci a kwantar da hankula a Sudan ta kudu
2016-07-03 12:16:16 cri
Wani jami'in hukumar bada agaji a Sudan ta kudu ya bukaci bangarorin da basa ga maciji da juna dasu dakatar da fadan da suke a yankin Wau, sannan ya bukaci a kyale jami'an bada agaji su shiga yankin arewa maso yammacin kasar domin kai kayan agaji ga mutanen dake cikin halin kuncin rayuwa.

Jami'in bada jin kan Eugene Owusu, wanda ya kai ziyarar wuni guda yankin na Wau a ranar Alhamis, ya bayyana damuwa game da irin hasarar rayuka da ake samu a yankin, baya ga fararen hula da rikicin ya tilastawa barin gidadjen su da kuma wadanda suka fada cikin mawuyacin hali sakamakon rikicin.

Owusu ya fada a Juba cewa, wannan ba abu ne da za'a lamunce da shi ba. A cewarsa dole ne jami'an tsaro su tashi tsaye don sauke nauyin dake wuyansu na kare rayukan fararen hula da dakatar da duk wasu nau'oin hare hare a yankin.

Jami'in ya nuna damuwa matuka game da barkewar fadan tun daga ranar 24 ga watan Yuni, lamarin da ya haddasa mutuwar sama da mutane 40, sannan ya tilastawa a kalla mutane 70,000 barin gidajensu.

Bugu da kari kimanin mutane 12,000 ne ke neman mafaka a kusa da ofishin MDD dake jamhuriyar Sudan ta kudu wanda ke yankin na Wau.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China