in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sudan ta kudu ta gano ma'adanan gwal da tagulla da tama
2016-06-13 10:46:35 cri
Ministan ma'adanai na Sudan ta kudu Taban Deng ya ce kasarsa ta gano wasu tarin ma'adanai a wasu yankunan kasar, kuma kashi 44 na yankunan kasar na dauke da ma'adanan da suka hada da gwal, da tagulla da sauran ma'adai masu daraja.

Deng ya ce akwai kwararan shedu dake tabbatar da cewar kaso 44 na yankunan Sudan ta kudun na da ma'adanan makare a karkashin kasa musamman zinare da tama da sauran ma'adanai masu daraja.

Ministan ya bayyana hakan ne a lokacin da yake ganawa da ministan ma'adanai na kasar Sudan Ahmed Muhammad Sadiq Al-Kanuri a birnin Khartoum.

Deng ya ce ya ziyarci Sudan ne domin samun muhimman bayanai game da yanayin taswirar Sudan ta kudu wadda a baya yanki ne daga kasar Sudan wanda ya balle a shekarar 2011.

A nasa jawabin ministan ma'adanai na Sudan ya shedawa 'yan jaridu cewar a shirye yake ya ba da muhimman bayanan da suka dace ga Sudan ta kudun. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China