in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dream Team ta fara samun horo a Amurka
2016-06-29 10:32:35 cri
Kungiyar wasan kwallon kafata ta Najeriya da aka kafa musamman domin wasannin Olympics dake tafe, wadda aka fi sani da suna "Dream Team" , yanzu haka tana samun horo a kasar Amurka. Daga can ne kuma za su tashi zuwa kasar Mexico inda za su halarci wani wasan sada zumunta a ranar 2 ga wata mai zuwa.

Kafin haka babban kocin kungiyar Samson Siasia ya riga ya tabbatar da 'yan wasa 35 ne za su halarci Rio Olympics a watan Augusta. Haka kuma ana saran ganin daga cikin wadannan 'yan wasan, galibin wadanda ke taka leda a kasashen waje za su koma sansanin horaswa da kungiyar ta kafa a Atlanta na kasar Amurka.

Sai dai a nata bangaren, kulob din Manchester City ta ce ba zata yarda da dan wasan gabanta Kelechi Iheanacho, ya halaci wasannin Olympics na wannan karo ba, duk da cewar hadaddiyar kungiyar wasan kwallon kafan Najeriya NFF ta riga ta sanya sunan dan wasan mai shekaru 18 a duniya cikin jerin sunayen 'yan wasa 35 da za su shiga wasannin Olympics.

Kafafen yada labaru na kasar Birtaniya sun bayyana cewa, kulob din Manchester City na son sanya Iheanacho da sauran 'yan wasan kulob din zama tare da sabon kocin Pep Guardiola duk tsawon watanni kafin a fara wani sabon kakar wasanni, don haka ba zai yiwu ba ta bar dan wasan Najeriya ya tafi Brazil a wani lokacin da ake dab da fara wasannin Premier League.

Sai dai an ce niyyar da Man. City ta tsayar ba ta karya doka ba, ganin kulob na da ikon hana 'yan wasanta zuwa halartar sauran wasanni, idan har ta ga babu damar yin hakan.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China