in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Najeriya sun kubutar da mutane 5000 a jihar Borno
2016-06-27 10:47:36 cri
Sojojin Najeriya da ke gudanar da ayyuka a jihar Borno dake arewa maso gabashin kasar sun sanar a jiya Lahadi cewa, sun ceto mutane fiye da 5000, wadanda 'yan Boko Haram suka yi garkuwa da su.

Kakakin rudunar sojan Najeriya Kanar Sani Usman, ya bayyana haka ne cikin wata sanarwarsa, inda ya ce, sojojin runduna ta 21 da hadin gwiwar matasa 'yan sa kai sun kaddamar da simame kan kauyuka fiye da 10, inda suka hallaka 'yan Boko Haram 6 gami da raunata wasu da dama.

Ban da haka kuma, bisa matakan da suka dauka, sojojin gwamnati sun kwato motoci 5 da kekunan hawa 5 daga hannun 'yan Boko Haram, in ji kakakin.

Tun bayan da mayakan kungiyar Boko Haram suka fara tada zaune-tsaye a shekarar 2009, hare haren da suka kaddamar sun haddasa hasarar rayukan mutane fiye da 10,000, musamman ma a yankin arewa maso gabashin Najeriya.

Sojojin Najeriya da jami'an tsaro a matakai daban daban na kasar sun bayyana samun nasarori a kokarin su na murkushe dakarun kunigyar Boko Haram cikin shekarar da ta wuce, inda suka kwaci yawancin yankunan da kungiyar ta taba karbe ikon su a baya.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China